Mutum ɗaya ya rasa ransa a arangama tsakanin ‘yan sanda da mazauna garin Ibadan na Jihar Oyo, sakamakon zanga-zangar da suka yi kan ƙarancin takardun naira.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar yayin da ɗaruruwan mutanen suka hau kan tituna don nuna ɓacin ransu game da ƙarancin kuɗin, wanda ya shafi ƙasar baki ɗaya bayan sauya takardun N1,000 da N500 da N200.
Karanta Wannan: ICPC ta damke manyan jami’an Banki da suka boye Naira
Tun a ranar Juma’a wasu matasa suka farfasa tagogin wani banki da shaguna a Ibadan ɗin.
Cikin wata sanarwa, kakakin ‘yan sanda a Oyo, Adewale Osifeso, ya ce mutumin ya gamu da ajalinsa ne da misalin ƙarfe 10:15 na safe lokacin da jami’an tsaro ke gudanar da samamen haɗin gwiwa a yankin Apata na Ƙaramar Hukumar Ido.
Osifeso ya ce an bayyana mutumin a matsayin ɗan banga, kuma yana cikin waɗanda suka kai wa jami’an tsaron hari a lokacin samamen.