fidelitybank

Mutum daya ya mutu bakwai sun jikkata a rushewar ginin Kano

Date:

An kammala aikin ceto a wajen da wani bene mai hawa uku da ya rushe a kasuwar Beirut da ke Jihar Kano, inda gini ya danne mutane da dama.

Jami’an agajin gaggawa sun ce mutum daya ya mutu a baraguzan gini yayin da bakwai kuma suka samu raunuka, inda aka garzaya da su zuwa asibiti domin basu kulawa da ta dace.

Sai dai hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA, ta ce daya daga cikin wadanda suka samu raunuka ya samu karaya kuma yana asibiti ana kula da shi.

Hukumar ta NEMA ta fadawa BBC cewa ta kammala aikin ceto zuwa yanzu kuma babu sauran mutane da ke karkashin baraguzan gini.

Benen wanda yake dauke da shaguna da dama ba a kammala gina shi ba kafin ya rushe a jiya Talata. Ba a dai san me ya haddasa rushewar ginin ba.

Ana yawaita samun rushewar gine-gine a biranen Najeriya da ke janyo asarar rayuka, inda sau da dama ake dora laifin hakan a kan rashin bin ka’idojin gini da mutane basa bi.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp