An samu rahoton mutuwar mutum daya, yayin da wani kuma ya samu raunuka, bayan da wani kwale-kwalen da ke dauke da ‘yan kasuwa 50 daga Shiroro zuwa Kasuwar Kwata da ke Zumba a karamar hukumar Shiroro ta Jihar Neja ya kife a tsakiyar kogin Zumba.
Aminiya ta tattaro cewa, mutum shida ne kawai aka ceto daga cikin fasinjojin, kuma an tabbatar da mutuwar mutum daya.
An bayyana cewa hatsarin ya afku ne da yammacin ranar Asabar.
Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Ibrahim Inga, ya tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin, sai dai ya ce bai samu cikakken bayani kan asarar rayuka ba.
Sarkin Ruwa, Kwata-Zumba, Umar Isah, ya shaida cewa, injin kwale-kwalen da ke jigilar ‘yan kasuwar da suka hada da mata, yara, shanu, awaki da dama, kwandunan kifi da amfanin gona ya ruguje a tsakiyar kogin. .
Ya tabbatar da cewa ,daya daga cikin fasinjojin ya rasa ransa yayin da aka ceto wasu 6 da ransu, inda ya ce an yi asarar shanu 3 da awaki da sauran kayayyaki.