fidelitybank

Mutum daya ya mutu a cikin mutane hamsin da suka nutse a cikin Kogin Neja

Date:

An samu rahoton mutuwar mutum daya, yayin da wani kuma ya samu raunuka, bayan da wani kwale-kwalen da ke dauke da ‘yan kasuwa 50 daga Shiroro zuwa Kasuwar Kwata da ke Zumba a karamar hukumar Shiroro ta Jihar Neja ya kife a tsakiyar kogin Zumba.

Aminiya ta tattaro cewa, mutum shida ne kawai aka ceto daga cikin fasinjojin, kuma an tabbatar da mutuwar mutum daya.

An bayyana cewa hatsarin ya afku ne da yammacin ranar Asabar.

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Ibrahim Inga, ya tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin, sai dai ya ce bai samu cikakken bayani kan asarar rayuka ba.

Sarkin Ruwa, Kwata-Zumba, Umar Isah, ya shaida cewa, injin kwale-kwalen da ke jigilar ‘yan kasuwar da suka hada da mata, yara, shanu, awaki da dama, kwandunan kifi da amfanin gona ya ruguje a tsakiyar kogin. .

Ya tabbatar da cewa ,daya daga cikin fasinjojin ya rasa ransa yayin da aka ceto wasu 6 da ransu, inda ya ce an yi asarar shanu 3 da awaki da sauran kayayyaki.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp