fidelitybank

Mutum biyu sun yanke jiki sun mutu a lokacin da suke bin layin mai

Date:

Akalla mutane biyu a Sri Lanka sun mutu a lokacin da suke jiran dogayen layukan neman mai, yayin da karancin abinci ya haifar da zullumi da wahala a fadin kasar.

Kasar Sri Lanka na fama da matsalar tattalin arziki mafi muni a tarihinta a matsayinta na kasa mai cin gashin kanta, tare da rashin samun kudaden waje, domin siyan muhimman kayayyaki da ake shigowa da su kasar yana raguwar samar da muhimman kayayyaki.

A na tilastawa masu ababen hawa su jira sa’o’i a wajen gidajen mai, domin samun mai sannan gwamnati ta sanya dokar hana fita, saboda kamfanonin wutar lantarki ba su iya biyan isassun man fetur daga kasashen waje domin biyan bukata.

‘Yan sanda sun ce, wani dattijo mai shekaru 70 da ke kan layi domin siyan mai ya fadi kuma ya mutu a wani gidan mai da ke wajen babban birnin kasar Colombo ranar Lahadi.

Wannan dai shi ne karo na biyu da irin wannan mutuwa a cikin kwanaki da dama, bayan da wani dattijo ya fadi a garin Kandy a lokacin da yake jiran man kananzir ya yi amfani da shi, kamar yadda ‘yan sanda a birnin suka tabbatar.

Kafofin yada labaran cikin gida sun ce, wasu mata da dama da ke tsaye a cikin rana mai zafi domiin sayen gas sun suma a wurare da dama a tsibirin a karshen mako.

Masu jigilar man fetur da iskar gas sun yi zaman dirshan a babban tashar jiragen ruwa na Colombo, inda masu shigo da kaya suka kasa zayyano isassun kudaden kasashen waje domin biyan su.

Barkewar cutar ta Covid-19 ta durkusar da bangaren yawon shakatawa na Sri Lanka – babban mai samun kudin waje – kuma kudaden da ma’aikatan kasashen waje ke aikawa su ma sun ragu.

Hukumomin kasar sun sanar a makon da ya gabata cewa kasar za ta nemi tallafin IMF, don magance matsalar basussukan kasashen waje da ke kara tabarbarewa da kuma tara kudaden ajiyarta.

Hukumomin kididdigewa da masu sharhi na kasashen waje sun nuna shakku kan ikon da kasar da ke da karancin kudi na iya biyan bashin da ta ke bi na dala biliyan 51 a waje, tare da biyan dala biliyan 6.9 a bana.

Karancin ya yi barna a kusan kowane fanni na rayuwar yau da kullum, inda a wannan makon hukumomi suka dage jarabawar wa’adin dalibai kusan miliyan uku.

Kamfanin samar da wutar lantarki na tsibirin ya kuma ce, ba ya da takarda don buga takardun kudi na wata-wata ga miliyoyin masu amfani da su.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miÆ™a saÆ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe Æ´an É—aurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin Æ´an Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp