An tabbatar da mutuwar mutum biyu a ƙaramar hukumar Obi ta jihar Nasarawa a ranar Lahadi bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin soja da ɗansa da ke aiki a ofishin ƴansanda na Jenkwe a kasuwar Agyaragu.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansanda jihar, DSP Rahman Nansel ya fitar a ranar Lahadi, ya ce rikicin ya biyo bayan sace wani babur da aka yi.
Sanarwar ta ce, bayan an kai rahoton satar, sai ƴansanda suka kama wanda ake zargi tare da taimakon wani ɗansandan sarauniya da ke aiki a ƙarƙashin ofishin.
A lokacin da aka ɗauko wanda ake zargin za a tafi ofishin, sai wani soja wanda ke aiki a jihar Borno, amma ya zo hutu, ya tare ƴansanda domin hana su tafiya da wanda ake zargin.
“Ana cikin hakan ne aka ci ƙarfin sojan, sannan rikici ya ɓarke, har dukansu suka samu raunuka da ɗansandan sarauniyar, amma daga baya sai sojan ya rasu,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta ƙara da cewa daga baya wasu matasa sun zo sun ƙone ofishin ƴansanda, kamar yadda Channels ta ruwaito.