fidelitybank

Mutum biyu sun rasa ransu bayan kifewar kwale-kwale a Rimin Gado

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar mutane biyu a cikin wani kogi, bayan da kwale-kwalen su ya nutse a Zangon Durgu zuwa kauyen Kanya da ke karamar hukumar Rimin Gado.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na hukumar, SFS Saminu Yusif, ya ce, an ceto biyu da ransu, yayin da wasu biyu kuma suka rasa rayukansu nan take.

Ya ce, jami’an kashe gobara sun dauki matakin gaggawa ne, bayan da suka samu kira daga wani Barista Munir Dahiru, wanda ya kai musu rahoton faruwar lamarin da karfe 12:30 na ranar Litinin.

Ya kuma ce, mutane hudu ne lamarin ya rutsa da su, wanda suka ceto biyu sai dai kuma Sani Shitu mai shekaru 25 da Jabir Sabiu mai shekaru 30 sun rasa ransu a cikin ruwan.

Wadanda aka ceto sun hada da Sha’aban Bala mai shekaru 35 da Rabiu Bashari mai shekaru 30 a duniya, wanda suka mika su ga mataimakin shugaban karamar hukumar Rimin Gado, Shafi’u Abdullahi Gulu domin tattaunawa da alakar su domin daukar mataki na gaba.

Yusif ya kuma shawarci daukacin mutanen da ke amfani da kwale-kwale da su yi taka tsan-tsan ta hanyar yin amfani da jirgin ruwan a yankunan su.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp