fidelitybank

Mutum biyu sun rasa ransu bayan kifewar kwale-kwale a Rimin Gado

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar mutane biyu a cikin wani kogi, bayan da kwale-kwalen su ya nutse a Zangon Durgu zuwa kauyen Kanya da ke karamar hukumar Rimin Gado.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na hukumar, SFS Saminu Yusif, ya ce, an ceto biyu da ransu, yayin da wasu biyu kuma suka rasa rayukansu nan take.

Ya ce, jami’an kashe gobara sun dauki matakin gaggawa ne, bayan da suka samu kira daga wani Barista Munir Dahiru, wanda ya kai musu rahoton faruwar lamarin da karfe 12:30 na ranar Litinin.

Ya kuma ce, mutane hudu ne lamarin ya rutsa da su, wanda suka ceto biyu sai dai kuma Sani Shitu mai shekaru 25 da Jabir Sabiu mai shekaru 30 sun rasa ransu a cikin ruwan.

Wadanda aka ceto sun hada da Sha’aban Bala mai shekaru 35 da Rabiu Bashari mai shekaru 30 a duniya, wanda suka mika su ga mataimakin shugaban karamar hukumar Rimin Gado, Shafi’u Abdullahi Gulu domin tattaunawa da alakar su domin daukar mataki na gaba.

Yusif ya kuma shawarci daukacin mutanen da ke amfani da kwale-kwale da su yi taka tsan-tsan ta hanyar yin amfani da jirgin ruwan a yankunan su.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp