‘Yan sanda a kasar Jamus sun kama wani ɗan ƙasar Saudiyya bayan da wata mota ta afka cikin masu sayayya a wata kasuwar Kirsimeti mai cike da cunkoson jama’a a gabashin birnin Magdeburg.
Hotuna a kafafen sada zumunta sun nuna yadda motar ta shige rumfunan kasuwar a guje.
Shugaban, Rainer Haseloff ya ce wannan bala’i ne da ya faɗa wa birnin Magdeburg da ma ƙasar Jamus baki ɗaya.
Ya zuwa yanzu, mutum biyu sun mutu sannan da dama sun jikkata.
Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da ake kai hare-hare da mota tare da kashe mutane a kasuwar ta Kirsimeti a Jamus
Ko a shekarar 2016, wani mutum mai alaƙa da ƙungiyar IS ya kutsa da mota cikin wata kasuwar Kirsimeti a birnin Berlin tare da kashe mutum 12.