fidelitybank

Mutum biyar sun mutu bayan da jirgin sama ya yi karo da juna a Japan

Date:

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito ministan sufuri na Japan na tabbatar da mutuwar mutum biyar da ke cikin jirgin tsaron gaɓar teku da ya yi karo da wani jirgin fasinja da ya kama da wuta.

Kafar yaɗa labarai ta NHK ma ta ba da rahoton mutuwar mutanen biyar.

Direban jirgin ya samu tsira sai dai ya ji mummunan rauni.

Ana tunanin jirgin da ke gadin gaɓar tekun yana kai kayan abinci zuwa yankunan da girgizar ƙasa ta shafa lokacin da ya yi taho mu gama da jirgin kamfanin Japan Airlines lokacin da yake sauka kan titin jirgi.

Bayanai sun nuna cewa wani jirgin kamfanin Japan Airlines ya kama da wuta a lokacin da yake ƙoƙarin sauka a filin jirgin sama na Haneda da ke Tokyo a ranar Talata.

Wani bidiyo daga kafar yaɗa labarai ta NHK ya nuna yadda hayaƙi ke fitowa daga tagogin jirgin saman da kuma ta ƙasansa.

An kuma ga wutar na ci har a kan titin jirgin.

Kafar yaɗa labaran ta NHK ta ruwaito hukumomi na cewa wataƙila jirgin ya yi karo ne da wani jirgin bayan ya sauka a Haneda.

Akwai fasinjoji a cikin jirgin.

Kafar ta kuma ruwaito cewa jirgin ƙirar JAL 516 ya tashi ne daga Hokkaido.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp