fidelitybank

Mutum 7 sun mutu 100 sun jikkata a Ogun – FRSC

Date:

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), reshen jihar Ogun, ta bayyana a ranar Lahadi cewa, mutane bakwai ne suka mutu, yayin da wasu 100 suka jikkata a hadarurruka 41 da aka samu a yayin bikin Eid-el-Kabir na Sallah a jihar.

Kwamandan sashin, Ahmed Umar, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa (NAN) a Ota cewa, jami’an hukumar sun ceto mutane 195 da hadarin ya rutsa da su ba tare da sun ji rauni ba a cikin wannan lokaci.

Umar ya ce, jami’an sintiri na musamman na FRSC ne suka gudanar da aikin ceton daga ranar 6 ga watan Yuli zuwa 13 ga watan Yuli.

Kwamandan sashin ya kara da cewa, motoci 71 ne suka hadu da hatsarin guda 41 a lokacin bikin Sallah.

“Yawancin hadarurrukan sun faru ne saboda saba ka’idojin zirga-zirga.

“Masu ababen hawa na bukatar su rika bin ka’idojin zirga-zirga a koda yaushe, domin hana afkuwar hadurran da za a iya kaucewa a kan babbar hanya,” in ji shi.

Umar ya ce, hukumar za ta ci gaba da wayar da kan masu ababen hawa ta hanyar wayar da kan jama’a daban-daban kan tuki lafiya.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya ba za ta karbi ‘yan ciranin Venezuela ba da Amurka za ta ba mu – Najeriya

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya ce ƙasar...

Bafarawa ya kafa sabuwar kungiya

Wasu shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki daga...

An fara shirye-shiryen aikin Hajjin badi a Najeriya

Hukumar Alhazan Najeriya ta fara shirhin aikin hajjin 2026...

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne...

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Ministar al'adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya...

Rashin abinci mai gina jiki Najeriya ce kan gaba a Afirka ta biyu a duniya

Babbar mai taimaka wa shugaban Najeriya Bola Tinubu kan...

Gwamnatin Najeriya ta ciyo bashin dala miliyan 747

Najeriya ta karɓo bashin dala miliyan 747 daga bankunan...

Ba don Tinubu ba ko zaɓen fitar da gwani Buhari ba zai ci ba

Babban mai taimaka wa Shugaba Tinubu kan kafofin yaɗa...

Majalisa ta gayyaci Gwamnan Filato kan tsaron jihar

Kwamitin wucin gadi kan matsalolin tsaron jihar Filato na...

Sojoji sun sun kashe ‘yan Boko Haram 24

Rundunar Sojoji ƙarƙashin rundunar 'Operation Hadin Kai' mai yaƙi...

Dangote zai gina rumbum man fetur da dizel a Namibia

Matatar mai ta Dangote da ke Najeriya za ta...

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...
X whatsapp