Mutum shida ne kawai daga cikin 20 masu neman shugabancin kasar nan a karkashin jam’iyyar APC mai mulki suka sayi fom din tsayawa takara, kamar yadda rahotanni suka bayyana a jiya.
Haka kuma, ‘yan takarar gwamna a kasa 63 ne suka sayi fom din tsayawa takara.
A ranar Talata 26 ga watan Afrilu ne jam’iyya mai mulki ta fara sayar da fom din tsayawa takara ga ‘yan takarar shugaban kasa da na gwamna da na tarayya a ranar Juma’a 6 ga watan Mayu.
‘Yan takarar shugaban kasa guda shida sun hada da jagoran kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, da takwaransa na Ebonyi, Dave Umahi, da tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha da kuma karamin ministan ilimi Chukwuemeka Nwajiuba.