A jiya ne mutane hudu suka kone kurmus, yayin da wasu 13 suka samu raunuka a wani hatsarin mota daya tilo da ya afku a kusa da unguwar Fidiwo da ke kan hanyar Legas zuwa Ibadan a jihar Ogun.
Babban kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a jihar, Florence Okpe ta tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Abeokuta.
Ta ce hatsarin motar ya rutsa da fasinjoji 18 a cikin wata mota kirar Toyota HIACE, inda ta rasa yadda za ta yi a kan babbar hanyar, inda ta kama da wuta, ta kone mutum hudu da suka mutu, ba a iya gane su ba.
Okpe, wanda ya alakanta musabbabin hadarin da tsananin gudu da direban ya yi, ya ce tayar motar ta fashe tsabar gudu, kuma ta kama wuta bayan da ta yi karo da wata motar, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane hudun.
Ta kara da cewa an kai wadanda suka jikkata zuwa Asibitin Nasara da ke Ogere da sauran Asibitin Idera da ke Unguwar Sagamu a Jihar.
A halin yanzu, kwamandan hukumar FRSC Ogun, Umar Galadanci, ya jajantawa iyalan wadanda suka rasu. Ya shawarci masu ababen hawa da su rika tuka mota a hankali tare da duba tayoyinsu tare da gujewa keta gudu.