Wani mumunan hatsari ya afku a ranar Juma’a a jihar Bauchi, yayin da mutane uku suka rasa rayukansu, yayin da wasu 16 suka samu raunuka daban-daban a wani hatsarin mota.
Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira da aka yi da shi ranar Asabar a Bauchi.
A cewarsa, hatsarin ya rutsa da wata motar bas kirar Toyota Hiace ta jihar Jigawa ce, a kauyen Kurosha dake kan hanyar Bauchi zuwa Kano.
Kwamandan sashin, wanda ya bayyana cewa hatsarin ya afku ne da misalin karfe 6:13 na yamma, ya ce, jami’an hukumar sun dauki mintuna 8 da kyar kafin su isa wurin da hadarin ya afku, domin kai agaji.
Ya kuma daura laifin hatsarin a kan gudun wuce sa’a da kuma rashin kulawa.
“Mutane kusan 20 ne hatsarin ya rutsa da su, wadanda suka hada da manya maza 18, babba mace daya da kuma yarinya mace.
“Maza uku ne suka rasa rayukansu nan take, mutane 16, da suka hada da manya maza 15 da wata babbar mace sun samu raunuka, yayin da rai daya tilo da ba ta samu ba ita ce ‘yar mace,” in ji shi.
Abdullahi ya bayyana cewa duka gawarwakin mamacin da wadanda suka jikkata an kai su babban asibitin Ningi.