fidelitybank

Mutanen Osun ku tabbata an kidaya ku – Adeleke

Date:

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya yi kira ga mazauna jihar da su marawa hukumar kidaya ta kasa NPC baya, ta hanyar gabatar da kansu domin kidayar jama’a idan aka fara kirgen.

Za a fara ƙidayar yawan jama’a da gidaje ta ƙasa nan da 29 ga Maris, 2023.

Gwamna Adeleke ya yi wannan kiran ne a lokacin kaddamar da kwamitin bayar da shawarwari da aka kafa a hukumance a Osogbo.

Karanta Wannan: Karancin kudi zai kawo cikas wajen kidayar ‘yan Najeriya – Agba

Adeleke wanda mataimakinsa, Kola Adewusi ya wakilta, wanda ya bayyana fa’idodi da dama da ke tattare da kidayar jama’a, ya bayyana cewa hakan zai share fagen tsare-tsare da ci gaban kasa.

“Ina kira ga mazauna jihar Osun da su shiga cikin wannan atisayen domin samun moriyar jihar da za a iya samu daga kidayar gidaje da yawan jama’a.

“Ina kuma rokon hukumar NPC da ta kara amfani da lambar tantancewar bankin (BVN) da kuma gina ta domin tabbatar da samun saukin daukar adadi da bayanai,” in ji shi.

A nasa jawabin, kwamishinan NPC na jihar Osun, Sanata Mudasiru Hussein, ya bayyana shirin hukumar na fara kidayar jama’a da za ta kasance daidai, daidai kuma mai amfani ga kowa.

Shima da yake nasa jawabin, Daraktan NPC a jihar Osun, Martins Owoeye, ya bayyana cewa an yi kokarin ganin an yi kidayar jama’a da gidaje a shekarar 2023 ta bi ka’idojin kasa da kasa.

A cikin sakwannin fatan alheri da suka yi daban-daban, shugaban kungiyar ‘yan jarida ta Osun, NUJ, Wasiu Ajadosu; Daraktan hukumar wayar da kan jama’a ta kasa Kikelomo Ahmed; da wakilin kungiyar mata ta kasa, duk sun yi alkawarin ba da goyon baya don ganin an samu nasara.

An gudanar da kidayar jama’a da gidaje na karshe a Najeriya a watan Maris din shekarar 2006 a zamanin gwamnatin shugaba Olusegun Obasanjo. Kafin wannan lokacin, an yi kidayar karshe a shekarar 1991 karkashin mulkin Janar Ibrahim Babangida.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp