fidelitybank

Mutanen Ondo karku yi zaɓin tumun dare – Obi

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya yi kira ga masu zabe da kada su zabi kabilanci, sai dai su lura da halinsu.

Obi ya bayyana haka ne a ranar Asabar a Akure a wajen taron da aka yi na neman goyon bayan al’ummar jihar Ondo a zaben da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ya bayyana cewa shi da abokin takararsa, Ahmed Datti mutane ne da ake iya gano su, inda ya ce idan aka zabe su a matsayin shugaban kasa, ‘yan Najeriya za su yi alfahari da kasarsu kuma za su samu tsaro.

Obi wanda ya ce shi mai rowa ne amma ba ya cin hanci da rashawa, ya kara da cewa hakan ne ya sa zai iya ceto al’ummar jihar Anambra a matsayinsa na gwamna.

“Sun ce ni mai rowa ne, yanzu muna son masu rowa domin mu rike kudin. Muna so mu tabbatar mun yi amfani da kuɗin ku don sauya ƙasar.

“Kada ku zabi kabila, idan suka ce lokaci ne nasu, ku ce musu lokaci ne na ku don kwato kasar. A shirye muke mu ceto kasar.

“Wannan zaben ya shafi hali ne. Kun san tarihinmu, makarantar da muka je, ba mu san shekarun su ba,” inji shi.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp