fidelitybank

Mutanen Maiduguri su yi taka tsantsan da lafiyar su – Gwamnatin Borno

Date:

Gwamnatin jihar Borno ta yi gargaɗi ga mazauna birnin Maiduguri da suka fuskanci mummunar ambaliya, game da kiwon lafiyarsu.

Cikin wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labaran jihar ta fitar, ta yi kira ga al’umma su ɗauki matakan kare lafiyarsu da tsaron da muhimmanci fiye da komai.

Ma’aikatar ta zayyana wasu shawarwari da take son jama’a su kula da suka haɗa da:

Kauce wa saye ko sayar da ko kuma cin abincin da ya gurɓarta da ruwa ambaliya. Saboda a cewarta duk bincin da ya gurɓata da ruwan ambaliyar zai iya haifar da hatsari ga lafiya.

Sannan da saye ko sayar da ko cin naman dabbobin da suka mutu (Mushe), ”Kowane irin mushe na ƙunshe da guba”, a cewar ma’aikatar.

Hukumar ta kuma gargaɗi mutane su guji sace ko ɓarnatar da kayan gwamnati ko na wasu mutane.

Daga ƙarshe ta kuma yi kira ga mutane su kauce wa yin ninƙaya ko wanka a ruwan da ke tsaye.”Shi gurɓataccen ruwa koda an tafasa shi, ba za ka raba shi da matsalolin da za su iya yi wa lafiya illa ba”, kamar yadda ma’aikatar ta bayyana.

Ma’aikatar yaɗa labaran ta ce duk wanda aka samu da laifin fatali da waɗannan shawarwari zai fuskanci fushin hukuma.

A farkon makon da muke bankwana da shi ne dai wata mummunar ambaliya da ba ataɓa ganin irinta ba cikin sama da shekara 30, ta auka wa birnin Maiduguri, lamarin da ya shafi kusan mutum miliyan biyu a cewar gwamnan jihar.

Ambaliyar ta kuma yi sandin mutuwar aƙalla mutum 37, kamar yadda hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar NEMA ta bayyana.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp