fidelitybank

Mutanen Legas ku kwantar da hankalin ku – Sanwo-Olu

Date:

Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, ya yi kira ga jama’ar jihar da su kwantar da hankulansu kan fusatar da suka yi dangane da wahalhalun ƙarancin kuɗi da ake fuskanta a ƙasar.

Gwamnan ya yi wannan kira ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a fadar gwamnatin jihar da ke Marina, kan matsalar da ake ciki ta sauyin kuɗi a ƙasar.

Sanwo-Olu ya umarci mazauna jihar da su kauce wa duk wani tashin hankali, da zanga-zanga da ƙone-ƙone yana mai cewa hakan ba zai kawo mafita ga matsala ko wahalhalun da ake ciki ba

Ya ce “Ina mai jinjina a gare ku mutanen Legas dangane da haƙuri da juriya da kuka nuna a cikin wannan hali da ake ciki na tsaka-mai-wuya”.

“yan uwana al’ummar Legas, ina kira da tattausar murya a gare ku, a matsayina na gwamnanku, dan Allah ku kwantar da hankula a wannan lokaci, ku guji duk wani abu da zai tayar da hankali da zanga-zanga da kuma ƙone-ƙonea faɗin jiharmu”, in ji gamnan.

“Duk da wahalhalun da kowa ke ciki, tashin hankali ba zai zame mana mafita ba, duka mun sani cewa akwai mutanen da ke son yin amfani da tashe-tashen hankulan ta hanyar yin kalaman da ke tunzura jama’a”

”Kuma duk suna yin wannan ne da nufin hana ku damar kaɗa ƙuri’unku a zaɓen shugaban ƙasa, ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki, dan haka kada ku ba su dama su cimma manufarsu,”in ji Sanwo-Olu.

gwamnan ya ci gaba da cewa ba adalci ba ne kai hari kan dukiyoyin gwamnati da na al’umma.

A ranar Juma’a ne dai aka samu rahotonnin da ke cewa wasu fusatatun matasa sun toshe wasu titunan birnin Legas tare da ƙona tayoyi, sakamakon fusatar da suka yi kan ƙarancin takardun naira a ƙasar.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp