fidelitybank

Mutanen Kudu maso Yamma ku kada wa ‘yan takarar ku kuri’a – APC

Date:

Gabanin zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a ranar Asabar, jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ta yi kira ga al’ummar shiyyar Kudu maso Yamma da su kada kuri’a ga ‘yan takarar jam’iyyar.

Musamman jam’iyyar mai mulki ta bukaci mazauna jihohin Ogun, Legas, da Oyo da su marawa ‘yan takarar APC baya.

An yi wannan kiran ne a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Akure, babban birnin jihar Ondo, ta hannun Hon. Isaac Kekemeke, mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa (South-west).

Karanta Wannan: Mu na jan kunnen mutanen mazauan Legas – ‘Yan Sanda

Jigon na jam’iyyar APC ya yabawa ‘yan Najeriya daga dukkan yankuna kan goyon bayan zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya kuma bukaci yankin Kudu maso Yamma da su marawa ‘yan takarar jam’iyyar baya a zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki na ranar 11 ga watan Maris.

Kekemeke, tsohon sakataren gwamnatin jihar, SSG, kuma shugaban hukumar shirya jarabawa ta kasa NECO, ya bayyana cewa al’ummar kudu maso yamma za su ci gajiyar shugabancin Tinubu idan suka yi amfani da kuri’unsu wajen kafa gwamnonin APC da ‘yan majalisar jiha a jihohinsu. .

Ya kuma bayyana kwarin guiwa kan iyawa da kuma niyyar shugaban kasa na canza ruwayar da kuma rage wahalhalun da kasar ke fuskanta a halin yanzu sakamakon karancin naira.

Kekemeke, ya kuma yi kira ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, da ta samar da daidaito ga dukkan ‘yan takara a lokacin zabe mai zuwa.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp