Fitaccen mawakin nan Wizkid, ya nemi afuwa, saboda rashin zuwansa wasa Ghana kamar yadda ya tsara.
Wizkid, wanda sunansa na ainihi Ayodeji Ibrahim Balogun, ya kamata ya yi wasa a filin wasa na Accra a ranar Asabar.
To amma bai samu damar zuwa ba abin da ya fusata ‘yan kasar ciki har da wadanda suka shafe sa’oi a filin wasan suna jiran zuwansa.
Wadanda suka shirya wasan sun zargi mawakin da saba alkawari.
To amma a ranar Lahadi da daddare, mawakin ya nemi afuwar mutanen da suka shirya wasan dama wadanda suka shafe sa’oi suna jiran zuwansa, inda ya yi alkawarin samu ware wani lokaci a gaba don zuwa kasar ya yi wasa.