Wadanda suka cancanci kada kuri’a sun fara kada kuri’unsu a wasu sassan karamar hukumar Bwari da ke Abuja.
Atisayen wanda ya fara da misalin karfe 8 na safe, ya samu fitowar jama’a da dama wadanda suka sha alwashin ci gaba da kasancewa a rumfunan zabensu daban-daban domin tabbatar da an kirga kuri’unsu.
DAILY POST ta ziyarci wasu rumfunan zabe inda ta tattaro cewa jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC na nan a waje yayinda aka ci gaba da gudanar da zaben cikin lumana.
Wani mai kada kuri’a, Innocent Agaba, wanda ya zanta da wakilinmu a wata rumfar zabe da ke bayan Makarantar Lauyoyi, Bwari, ya ce shi ne mutum na farko da ya kada kuri’arsa a yankin.
Ya bayyana fatansa na cewa atisayen zai kare kamar yadda ake tsammani.
“Ya zuwa yanzu, abin yana tafiya yadda ya kamata. Ni ne mutum na farko da ya fara kada kuri’arsa a wannan rumfar zabe.
“Na zabe amma ba zan je ko’ina ba har sai an kirga kuri’a”, in ji shi.