fidelitybank

Mutane su guji gina gidaje a kan hanyar ruwa – Zulum

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya bayyana takaicinsa a kan yadda mutane suke gina gidaje a magudanar ruwa a jihar.

Zulum ya bayyana haka ne a ranar Alhamis bayan ya kai ziyarar duba ɓarnar da ambaliyar – wadda ta ɗaiɗaita jihar – ta yi ga hanyoyin mota da gadoji da asibitoci da sauransu.

A cewarsa, “Ɓarnar ta yi yawa. Mun ziyarci wurare da dama mun gani. Akwai ban takaici yadda mutane suke gina gidaje a magudanar ruwa. Ba don a tare masa hanya ba, da ruwan zai riƙa bin hanyarsa yana wucewa ne.

“Duk da gargaɗin da ake yi, amma har yanzu mutane suna cigaba da gini a magudanar ruwa, wanda irin waɗannan matsalolin ne suka jawo ambaliyar. Ba za mu watsar da kula da rayuwar mutanen Maiduguri ba saboda wasu ɗaiɗaikun mutane,” in jij shi kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

A ƙarshe ya yi kira ga ma’aikatar aikace-aikace da jami’an tsaro su tabbatar babu wanda ya sake yin gini a magudanar ruwa a jihar.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp