fidelitybank

Mutane shida sun mutu bayan kifewar Amalanke a ruwan jihar Jigawa

Date:

Aƙalla mutum shida ne suka mutu bayan kifewar amalanke a cikin wani rafi da ke yankin Gantsa na jihar Jigawa.

Jam’in yaɗa labarai na ƙaramar hukumar Buji, Ali Safiyyanu ya tabbatar wa BBC da afkuwar lamarin.

Ya ce bayan an gama aikin ceto ne da kuma fitar da waɗanda suka faɗa cikin ruwan ne aka garzaya da su babban asibitin Gantsa inda aka tabbatar da mutuwar mutanen.

Ya ƙara da cewa adadin mutanen da suka faɗa cikin ruwa sun kai mutum 10 inda tuni aka sallami huɗu yayin da kuma matuƙin amalanken ke ci gaba da karɓar magani a asibiti.

Ya kuma ce cikin waɗanda suka rasu, har da yara biyu da suka ƙwace daga hannun iyayensu.

“Mutanen sun faɗa cikin ruwan ne sakamakon karyewar amalanke.”

“Tun bayan da ruwa ya cinye hanyar da mutane ke bi ne ake amfani da amalanke da kwale-kwale wajen tsallakawa”.

“Ana tsallakawa da su ne daga Gantsa zuwa wani ruwa da ake tsallakawa domin a hau mota a tafi Sara inda akwai wata kasuwa da ke ci a duk ranar Talata.”

“Mutanen na cikin ruwan ne lokacin da sandar amalanke ta karye, saboda haka wasu suka tsorata inda suka yi yunƙurin fita sai kuma amalanken ya juye da su.” in ji jami’in

Ruwan sama mai yawa da ake samu a yankunan Najeriya ya sanya an samu ambaliya a sassa da dama, lamarin da ya haifar da katsewar hanyoyin sufuri sanadiyyar ɓallewar gadoji.

Ya zuwa yanzu Hukumar kai agajin gaggawa ta Najeriya ta tabbatar cewa aƙalla mutum 49 ne suka rasa rayukansu a fadin ƙasar.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp