fidelitybank

Mutane ne za su yi min alƙalancin mulki na – Buhari

Date:

Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce ya mulki Najeriya da iyakar iyawar da Allah ya ba shi.

Buhari ya bayyana haka ne a tattaunawa da gidan talbijin na ƙasa (NTA). Sai dai ya ce ya bar wa mutane su yi alƙalancin ko ya yi ƙoƙari ko kuma akasin haka.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce harkokin cikin gida sun dabaibaye gwamnatinsa, har ta kai ba ya damuwa da al’amuran ƙasashen waje a matsayinsa na shugaban ƙasa.

Ya ce babban ƙalubalen da ya fuskanta a lokacin mulkinsa, shi ne batun rashin tsaro da ya addabi ƙasar.

Sai dai, ya ce bayan ƙoƙari da gwamnatinsa ta yi wajen kyautata tsaro, hakan ya janyo mutane daga ciki da wajen ƙasar zuwa don zuba jari.

Buhari ya ce bai yi ƙoƙarin azurta kanshi ba, kamar wasu hamshakan Najeriya, musamman ma ta hanyar mallakar filaye, da gidaje da kuma motoci lokacin da yake mulki.

“Dalilin haka ne ma ya sa nake rayuwata cikin kwanciyar hankali bayan na bar mulki,” in ji Buhari.

Ya ce wasu ƴan Najeriya sun yi yunƙurin kafa masa tarko ta hanyar ɓullo masa da abubuwa da yawa.

Ya ce: “Na yi ƙoƙarin kaucewa tarkon da suka ɗana min saboda na san cewa muddin suka samu nasara a kaina, to za su yi amfani da damar wajen tatse ƙasa.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp