fidelitybank

Mutane ne za su yi min alƙalancin mulki na – Buhari

Date:

Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce ya mulki Najeriya da iyakar iyawar da Allah ya ba shi.

Buhari ya bayyana haka ne a tattaunawa da gidan talbijin na ƙasa (NTA). Sai dai ya ce ya bar wa mutane su yi alƙalancin ko ya yi ƙoƙari ko kuma akasin haka.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce harkokin cikin gida sun dabaibaye gwamnatinsa, har ta kai ba ya damuwa da al’amuran ƙasashen waje a matsayinsa na shugaban ƙasa.

Ya ce babban ƙalubalen da ya fuskanta a lokacin mulkinsa, shi ne batun rashin tsaro da ya addabi ƙasar.

Sai dai, ya ce bayan ƙoƙari da gwamnatinsa ta yi wajen kyautata tsaro, hakan ya janyo mutane daga ciki da wajen ƙasar zuwa don zuba jari.

Buhari ya ce bai yi ƙoƙarin azurta kanshi ba, kamar wasu hamshakan Najeriya, musamman ma ta hanyar mallakar filaye, da gidaje da kuma motoci lokacin da yake mulki.

“Dalilin haka ne ma ya sa nake rayuwata cikin kwanciyar hankali bayan na bar mulki,” in ji Buhari.

Ya ce wasu ƴan Najeriya sun yi yunƙurin kafa masa tarko ta hanyar ɓullo masa da abubuwa da yawa.

Ya ce: “Na yi ƙoƙarin kaucewa tarkon da suka ɗana min saboda na san cewa muddin suka samu nasara a kaina, to za su yi amfani da damar wajen tatse ƙasa.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp