Buhari ya bayyana haka ne a tattaunawa da gidan talbijin na ƙasa (NTA). Sai dai ya ce ya bar wa mutane su yi alƙalancin ko ya yi ƙoƙari ko kuma akasin haka.
Tsohon shugaban ƙasar ya ce harkokin cikin gida sun dabaibaye gwamnatinsa, har ta kai ba ya damuwa da al’amuran ƙasashen waje a matsayinsa na shugaban ƙasa.
Ya ce babban ƙalubalen da ya fuskanta a lokacin mulkinsa, shi ne batun rashin tsaro da ya addabi ƙasar.
Sai dai, ya ce bayan ƙoƙari da gwamnatinsa ta yi wajen kyautata tsaro, hakan ya janyo mutane daga ciki da wajen ƙasar zuwa don zuba jari.
Buhari ya ce bai yi ƙoƙarin azurta kanshi ba, kamar wasu hamshakan Najeriya, musamman ma ta hanyar mallakar filaye, da gidaje da kuma motoci lokacin da yake mulki.
“Dalilin haka ne ma ya sa nake rayuwata cikin kwanciyar hankali bayan na bar mulki,” in ji Buhari.
Ya ce wasu ƴan Najeriya sun yi yunƙurin kafa masa tarko ta hanyar ɓullo masa da abubuwa da yawa.
Ya ce: “Na yi ƙoƙarin kaucewa tarkon da suka ɗana min saboda na san cewa muddin suka samu nasara a kaina, to za su yi amfani da damar wajen tatse ƙasa.