fidelitybank

Mutane na yin tir da farwa Farfesa a jihar Adamawa

Date:

Mutane da dama a shafukan sada zumunta na ci gaba da yin Alla-wadai da far wa jami’an zaɓe a jihar Adamawa, ciki har da wani dattijon farfesa wasu suka yi wa jina-jina.

Ana dai ta kira ga hukumomi a kan su gaggauta kama waɗanda ake zargi kan wannan aika-aika, tare da gurfanar da su a kotu.

Farfesa Abdullahi Zuru dai ya kasance tsohon shugaban jami’ar Usman Danfodiyo ta jihar Sokoto, inda ya je aiki jihar Adamawa a matsayin jami’in INEC don cikon zaɓen gwamna da aka yi ranar Asabar.

Ita ma, ƙungiyar tsoffin ɗaliban Usman Danfodiyo ta yi Allah-wadai da cin mutuncin da aka yi wa farfesan.

Cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta yi kira ga hukumomi su gaggauta kamo waɗanda ake zargin don hukunta su.

A jiya Lahadi ne wani bidiyo ya riƙa nuna Farfesa Abdullahi Zuru, zaune jini ya ɓata sassan jikinsa.

Hukumar zaɓe ta tura shi ne jihar Adamawa a matsayin kwamishina a zaɓen cike giɓi wanda daga bisani ya zo da taƙaddama, lamarin da ya sa INEC ta dakatar da aikin sanar da sakamako.

Far wa Abdullahi Zuru ya zo ne bayan kwamishinan INEC a jihar ta Adamawa Barrister Hudu Ari, ya sanar da Aisha Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jihar duk da cewar ba a kammala tattara sakamakon ba a lokacin

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp