A yayin da ya rage ƙasa da mako takwas a gudanar da babban zaɓen 2023, Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce akwai aƙalla mutum miliyan 6.7 da ba su karɓi katunan zaɓensu ba.
Wani rahoto da ya fito daga ofisoshin INEC a jihohin ƙasar ranar Talata ya nuna cewa akwai katuna kusan miliyan 6.7 da ke ƙunshe cikin ofisohin INEC a jihohin ƙasar 17 da kuma babban birnin tarayyar ƙasar Abuja.
Tun da farko dai Hukumar Zaɓen mai Zaman ƙanta a Najeriya ta bayyana cewa za ta fara rabar da katunan zaɓen daga watan Disamban da ya gabata zuwa ranar 22 ga watan Janairun da muke ciki.
Babban kwamishinan hukumar kuma shugaban kwamitin yada labarai da ilimantar da masu kaɗa ƙuri’a, Festu Okoye ya faɗa a wata sanarwa da ya fitar cewa daga ranar 6 zuwa 15 ga watan Janairu za a mayar da katunan zuwa mazaɓu domin sauƙaƙa wa jama’a karɓar katin.