fidelitybank

Mutane miliyan 6.7 ba su karbi katin zaben su ba – INEC

Date:

A yayin da ya rage ƙasa da mako takwas a gudanar da babban zaɓen 2023, Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce akwai aƙalla mutum miliyan 6.7 da ba su karɓi katunan zaɓensu ba.

Wani rahoto da ya fito daga ofisoshin INEC a jihohin ƙasar ranar Talata ya nuna cewa akwai katuna kusan miliyan 6.7 da ke ƙunshe cikin ofisohin INEC a jihohin ƙasar 17 da kuma babban birnin tarayyar ƙasar Abuja.

Tun da farko dai Hukumar Zaɓen mai Zaman ƙanta a Najeriya ta bayyana cewa za ta fara rabar da katunan zaɓen daga watan Disamban da ya gabata zuwa ranar 22 ga watan Janairun da muke ciki.

Babban kwamishinan hukumar kuma shugaban kwamitin yada labarai da ilimantar da masu kaɗa ƙuri’a, Festu Okoye ya faɗa a wata sanarwa da ya fitar cewa daga ranar 6 zuwa 15 ga watan Janairu za a mayar da katunan zuwa mazaɓu domin sauƙaƙa wa jama’a karɓar katin.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp