Kimanin mutane miliyan 1.2 ne ke fuskantar barazanar tashin bama-bamai a jihohin Borno da Adamawa da Yobe.
Jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya Mista Matthias Schmale ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja.
Da yake jawabi a ranar wayar da kan ma’adanai da taimakon ma’adanai ta duniya ta shekarar 2022, Schmale na Hukumar Ba da Agaji da Ayyuka ta Majalisar Dinkin Duniya, ya ce, mutane miliyan 1.2 na bukatar agajin ceton rayuka a jihohin uku.
Ya ce, an gano wadanda ke cikin hatsarin yayin aiwatar da batun bukatun Jin kai na hukumar Majalisar Dinkin Duniya na shekarar 2022.
Ya lura cewa bama-bamai a nau’ikansu daban-daban na ci gaba da karin barazana ga al’ummomin da ke fama da wahala a Arewa maso Gabashin Najeriya.
Ya ce, Hukumar Kula da Ma’adanai ta Majalisar Dinkin Duniya (UNMAS) ta tattara al’amura 1,532 a yankin da suka shafi hadurran fashewa daga watan Janairun 2016 zuwa Janairun 2022 da suka shafi sama da 10,000.
Ya kara da cewa, kimanin fararen hula 1,356 ne suka jikkata, yayin da 789 suka mutu daga adadin wadanda aka samu.