fidelitybank

Mutane hudu yayin da goma suka jikkata bayan mota ta kone kurmus a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yansandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum huɗu da kuma jikkatar wasu 10 bayan wata motar bas ta kama da wuta.

Lamarin ya faru ne a ƙaramar hukumar Gwaram, kamar yadda kakakin rundunar Lawan Shiisu ya bayyana cikin wata sanarwa ranar Lahadi.

“Lamarin ya faru ne ranar Asabar da misalin ƙarfe 4:00 na yamma lokacin da bas ɗin da ke ɗauke da fasinjoji 44 daga garin Zaki na jihar Bauchi ta kama da wuta,” in ji shi.

“Bayan ta isa kusa da makarantar Government Girls Unity Secondary School Gwaram, sai wutar ta mamaye motar sakamakon haɗuwa da ta yi da wata katifa da aka ɗaure a bayan motar.”

Wutar ta ƙone mutanen ne duka mata ƙurmus ta yadda ba za a iya gane su ba, a cewarsa. Waɗanda suka ji raunika kuma, nan take aka garzaya da su asibitin Gwaram Cottage.

Ya ƙara da cewa daga cikin fasinjojin, 25 manya ne, da kuma yara 19.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp