Rundunar ‘yansandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum huɗu da kuma jikkatar wasu 10 bayan wata motar bas ta kama da wuta.
Lamarin ya faru ne a ƙaramar hukumar Gwaram, kamar yadda kakakin rundunar Lawan Shiisu ya bayyana cikin wata sanarwa ranar Lahadi.
“Lamarin ya faru ne ranar Asabar da misalin ƙarfe 4:00 na yamma lokacin da bas ɗin da ke ɗauke da fasinjoji 44 daga garin Zaki na jihar Bauchi ta kama da wuta,” in ji shi.
“Bayan ta isa kusa da makarantar Government Girls Unity Secondary School Gwaram, sai wutar ta mamaye motar sakamakon haɗuwa da ta yi da wata katifa da aka ɗaure a bayan motar.”
Wutar ta ƙone mutanen ne duka mata ƙurmus ta yadda ba za a iya gane su ba, a cewarsa. Waɗanda suka ji raunika kuma, nan take aka garzaya da su asibitin Gwaram Cottage.
Ya ƙara da cewa daga cikin fasinjojin, 25 manya ne, da kuma yara 19.