Wani fashewa da aka yi a wani wurin hakar ma’adinai a Sabon Pegi da ke cikin karamar hukumar Mashegun a jihar Neja ya yi sanadin mutuwar mutane hudu tare da jikkata wasu da dama.
Fashewar ta faru ne da safiyar Lahadi a yayin da masu hakar ma’adinai ke ci gaba da gudanar da aikinsu a wurin.
Yayin da har yanzu ba a tantance ainihin musabbabin fashewar ba, mazauna unguwar Sabon Pegi sun yi hasashen cewa rashin kula da ababen fashewa da kamfanonin hakar ma’adanai ke yi ya taimaka wajen faruwar lamarin.
Majiyoyin al’umma sun ruwaito cewa an tsamo gawarwaki hudu daga wurin fashewar, ko da yake ba a san cikakken adadin wadanda suka mutu ba, kuma ana fargabar karin wadanda suka mutu.
Har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba.
Har yanzu dai hukumomi ba su ce uffan ba game da lamarin.