fidelitybank

Mutane da dama sun yi mamakin yadda na zama kasurgumin dan ta’adda – Turji

Date:

Kasurgumin dan bindigar nan da ya addabi al’ummar yankuna su Zamfara da kewaye, Bello Turji, ya ce, asalinsa makiyayi ne kuma mutane suna mamakin yadda ya zama dan ta’adda mai garkuwa da mutane.

Turji, wanda dan asalin garin Fakai a karamar Shinkafi na jihar Zamfara ne, ya bayyana cewa, wadanda suka san shi sun yi mamakin yadda ya fara sata da kashe-kashe.

A wata hirar da ya yi da tashar Trust TV, Turji ya ce: “A baya ni makiyayi ne. Idan mahaifi na na son sayar da Shanunsa, ni ke kai masa kasuwa. Idan na sayar sai in tafi fadar Sarkin Shinkafi kafin in koma gida, kuma sarkin Shinkafi ya san ni. Idan a ka fada masa Turji zai zama dan bindiga, ba zai yarda ba, saboda ya san mu Fulani ba zamu zama barayin Shanu ba. Amma abubuwan da ake mana ya fara yawa.”

Turji ya kara da cewa, a rana guda aka kashe masa ‘yan uwa shida, bayan sacewa iyayensa Shanu sama da dubu. A cewarsa, sun je duk kotunan duniyan nan, amma Shanunsu basu dawo ba.

“An kwashe mana sama da Shanu 1000. A ranar, an kashe ‘yan uwana shida. Iyayenmu sun je kotu, amma a dawo musu da Shanunsu ba. Hakazalika an hada kai da ‘yan sa kai wajen kashe babban yayana. Ina talaka zai samu adalci?” in ji Turji.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp