fidelitybank

Mutane biyu sun mutu a wani sabon hari da aka kai Taraba

Date:

An sake tabbatar da mutuwar mutane biyu a wasu hare-haren da aka kai a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, wanda ya faru a ranar Juma’a, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar (PPRO), Abdullahi Usman, ya ce a farkon lamarin, ‘yan bindiga sun kai hari a wani gida, inda suka yi amfani da adduna suka farfasa tagar gidan.

A cewarsa, an harbe wata budurwa da ke karatun jarabawa a dakinta.

“Tana karatu a dakinta sai suka bude mata wuta, suka buge ta a baya. Harsashin ya fita ne ta cikinta,” Usman ya bayyana.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun umurci mazauna gidan da su fito waje amma ba su yi awon gaba da kowa ba balle su dauki wani abu mai daraja.

Lamarin na biyu a cewar rundunar ‘yan sandan ya faru ne a unguwar Jerbanbur da ke Jalingo, inda aka kai wa wani malamin addini hari.

Usman ya ce maharan sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi inda suka tafi ba tare da sun yi awon gaba da kowa ba.

Ya kara da cewa, “An garzaya da wadanda suka mutun zuwa asibiti amma sun mutu a lokacin da suke karbar magani.”

Rundunar ta bayyana hare-haren a matsayin wanda ba a saba gani ba, inda ta ce maharan ba sa bin tsarin garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

Rundunar ‘yan sandan, kamar yadda ya bayyana, ta kaddamar da kwakkwaran bincike domin ganowa tare da cafke wadanda ke da hannu a kisan.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp