An sake tabbatar da mutuwar mutane biyu a wasu hare-haren da aka kai a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, wanda ya faru a ranar Juma’a, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar (PPRO), Abdullahi Usman, ya ce a farkon lamarin, ‘yan bindiga sun kai hari a wani gida, inda suka yi amfani da adduna suka farfasa tagar gidan.
A cewarsa, an harbe wata budurwa da ke karatun jarabawa a dakinta.
“Tana karatu a dakinta sai suka bude mata wuta, suka buge ta a baya. Harsashin ya fita ne ta cikinta,” Usman ya bayyana.
Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun umurci mazauna gidan da su fito waje amma ba su yi awon gaba da kowa ba balle su dauki wani abu mai daraja.
Lamarin na biyu a cewar rundunar ‘yan sandan ya faru ne a unguwar Jerbanbur da ke Jalingo, inda aka kai wa wani malamin addini hari.
Usman ya ce maharan sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi inda suka tafi ba tare da sun yi awon gaba da kowa ba.
Ya kara da cewa, “An garzaya da wadanda suka mutun zuwa asibiti amma sun mutu a lokacin da suke karbar magani.”
Rundunar ta bayyana hare-haren a matsayin wanda ba a saba gani ba, inda ta ce maharan ba sa bin tsarin garkuwa da mutane don neman kudin fansa.
Rundunar ‘yan sandan, kamar yadda ya bayyana, ta kaddamar da kwakkwaran bincike domin ganowa tare da cafke wadanda ke da hannu a kisan.