Mutane biyu sun mutu a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan, a wani hatsarin da ya afku a ranar Juma’a.
Rahotanni sun rawaito cewa mutane 10 kuma sun jikkata a hatsarin wanda ya afku da misalin karfe 08:32 na safe.
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta ce mutane 14 ne suka yi hatsarin, “inda biyu suka mutu nan take, inda mutane 10 suka samu raunuka, wasu 2 kuma ba su samu raunuka ba.
A wata sanarwa da hukumar ta FRSC ta fitar ta hannun kakakinta a Ogun, Florence Okpe, ta ce hatsarin ya rutsa da wata farar motar bas ta Mazda mai lamba XV945EPE da kuma wata mota kirar Howo Sino mara rijista.
Okpe ya dora laifin hatsarin kan hanya da kuma tukin mota mai hatsari.
Ta kara da cewa an kai wadanda suka jikkata zuwa asibitin Famobis kuma an ajiye gawarwakin a dakin ajiye gawa na Idera.
A halin da ake ciki, kwamandan hukumar ta FRSC a jihar Ogun, Anthony Uga, ya shawarci direbobi da su guji tukin mota, inda ya bukaci su yi taka-tsan-tsan a lokacin da suke tuki domin gujewa jefa rayuwarsu da sauran masu amfani da hanyar cikin hadari.