Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja, NSEMA, ta tabbatar da mutuwar mutane bakwai a kananan hukumomin Magama da Rafi na jihar sakamakon ambaliyar ruwa.
Babban Daraktan NSEMA, Mal Ahmed Ibrahim Inga ne ya bayyana haka a Minna, ya kuma ce an samu mutuwar mutane shida a Magama, daya kuma a Rafi.
Shugaban hukumar NSEMA ya bayyana cewa jihar ta fara fuskantar mummunar illar da ambaliyar ta haifar, inda gidaje, gonaki, gadoji, da wasu hanyoyin da suka hada da suka tafi da su a wasu kananan hukumomin da ke sama da kasa na madatsun ruwa hudu.
Ya bayyana cewa, “Wadannan sun sa mutane da yawa sun rasa matsuguni kuma sun shafi ayyukan zamantakewa da tattalin arzikin al’umma. Kananan hukumomin sun hada da Lavun, Magama, Rafi, Kontagora, Gbako, Mashegu da Wushishi.”