fidelitybank

Mutane bakwai su ka mutu a zanga-zangar yunwa – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi alkawarin aiwatar da cikakken shawarwarin da kwamitin bincike kan zanga-zangar neman kawo karshen mugunyar mulki da aka gudanar a ranar 1 ga watan Agusta, 2024.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar ta bayyana cewa mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da aka lalata dukiyoyin da suka kai Naira biliyan 11 a yayin zanga-zangar.

Da yake karbar rahoton daga shugaban hukumar, Mai shari’a Lawan Wada (rtd), a yayin taron majalisar zartarwa ta jihar Kano karo na 25 a gidan gwamnati, gwamnan ya kuma bayyana cewa za a fitar da wata farar takarda, da za ta zakulo wadanda ke da alhakin daukar nauyin zanga-zangar da kuma haddasa tarzoma.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Talata, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewar rahoton, mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.

Bugu da kari, an lalata kadarorin gwamnati da na masu zaman kansu na sama da Naira biliyan 11 a zanga-zangar.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa ba ta tsoma baki a binciken da hukumar ta yi na tsawon watanni shida, wanda hakan ya baiwa mambobin ‘yancin cin gashin kansu su gudanar da ayyukansu da kyau.

“Ina da kwarin gwiwa kan gaskiya da kwarewar mambobin kwamitin.

“An zabo su ne bisa cancanta, kuma ina da kwarin gwiwar cewa sun yi aikinsu ba tare da nuna son kai ba,” in ji shi.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta dauki matakin da ya dace kan sakamakon rahoton domin ya zama tinkarar masu tada zaune tsaye da barna.

Ya kuma yabawa kwamatin kan aikin da aka yi, sannan ya bukace su da su kasance cikin shiri domin gudanar da ayyuka a nan gaba idan gwamnati ta bukaci kwararrun su.

Da yake gabatar da rahoton, Mai shari’a Wada ya bayyana cewa kwamitin ya ziyarci dukkan yankunan da abin ya shafa tare da hada hannu da masu ruwa da tsaki domin tattara cikakken bayani kan tasirin zanga-zangar.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp