Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi alkawarin aiwatar da cikakken shawarwarin da kwamitin bincike kan zanga-zangar neman kawo karshen mugunyar mulki da aka gudanar a ranar 1 ga watan Agusta, 2024.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar ta bayyana cewa mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da aka lalata dukiyoyin da suka kai Naira biliyan 11 a yayin zanga-zangar.
Da yake karbar rahoton daga shugaban hukumar, Mai shari’a Lawan Wada (rtd), a yayin taron majalisar zartarwa ta jihar Kano karo na 25 a gidan gwamnati, gwamnan ya kuma bayyana cewa za a fitar da wata farar takarda, da za ta zakulo wadanda ke da alhakin daukar nauyin zanga-zangar da kuma haddasa tarzoma.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Talata, ta tabbatar da faruwar lamarin.
A cewar rahoton, mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.
Bugu da kari, an lalata kadarorin gwamnati da na masu zaman kansu na sama da Naira biliyan 11 a zanga-zangar.
Gwamna Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa ba ta tsoma baki a binciken da hukumar ta yi na tsawon watanni shida, wanda hakan ya baiwa mambobin ‘yancin cin gashin kansu su gudanar da ayyukansu da kyau.
“Ina da kwarin gwiwa kan gaskiya da kwarewar mambobin kwamitin.
“An zabo su ne bisa cancanta, kuma ina da kwarin gwiwar cewa sun yi aikinsu ba tare da nuna son kai ba,” in ji shi.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta dauki matakin da ya dace kan sakamakon rahoton domin ya zama tinkarar masu tada zaune tsaye da barna.
Ya kuma yabawa kwamatin kan aikin da aka yi, sannan ya bukace su da su kasance cikin shiri domin gudanar da ayyuka a nan gaba idan gwamnati ta bukaci kwararrun su.
Da yake gabatar da rahoton, Mai shari’a Wada ya bayyana cewa kwamitin ya ziyarci dukkan yankunan da abin ya shafa tare da hada hannu da masu ruwa da tsaki domin tattara cikakken bayani kan tasirin zanga-zangar.