fidelitybank

Mutane bakwai su ka mutu a zanga-zangar yunwa – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi alkawarin aiwatar da cikakken shawarwarin da kwamitin bincike kan zanga-zangar neman kawo karshen mugunyar mulki da aka gudanar a ranar 1 ga watan Agusta, 2024.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar ta bayyana cewa mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da aka lalata dukiyoyin da suka kai Naira biliyan 11 a yayin zanga-zangar.

Da yake karbar rahoton daga shugaban hukumar, Mai shari’a Lawan Wada (rtd), a yayin taron majalisar zartarwa ta jihar Kano karo na 25 a gidan gwamnati, gwamnan ya kuma bayyana cewa za a fitar da wata farar takarda, da za ta zakulo wadanda ke da alhakin daukar nauyin zanga-zangar da kuma haddasa tarzoma.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Talata, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewar rahoton, mutane 10 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.

Bugu da kari, an lalata kadarorin gwamnati da na masu zaman kansu na sama da Naira biliyan 11 a zanga-zangar.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa ba ta tsoma baki a binciken da hukumar ta yi na tsawon watanni shida, wanda hakan ya baiwa mambobin ‘yancin cin gashin kansu su gudanar da ayyukansu da kyau.

“Ina da kwarin gwiwa kan gaskiya da kwarewar mambobin kwamitin.

“An zabo su ne bisa cancanta, kuma ina da kwarin gwiwar cewa sun yi aikinsu ba tare da nuna son kai ba,” in ji shi.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta dauki matakin da ya dace kan sakamakon rahoton domin ya zama tinkarar masu tada zaune tsaye da barna.

Ya kuma yabawa kwamatin kan aikin da aka yi, sannan ya bukace su da su kasance cikin shiri domin gudanar da ayyuka a nan gaba idan gwamnati ta bukaci kwararrun su.

Da yake gabatar da rahoton, Mai shari’a Wada ya bayyana cewa kwamitin ya ziyarci dukkan yankunan da abin ya shafa tare da hada hannu da masu ruwa da tsaki domin tattara cikakken bayani kan tasirin zanga-zangar.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp