fidelitybank

Mutane 9 sun kone kurmus a jihar Ondo – FRSC

Date:

Mutane 9 ne suka kone kurmus a ranar Juma’a, a wani hatsarin mota da ya afku a gadar Omotosho Step Down, kan titin Ore-Lagos a karamar hukumar Odigbo ta jihar Ondo.

Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) na rundunar Ore, Sikiru Alonge, wanda ya tabbatar da faruwar hatsarin, ya ce hadarin da ya faru da sanyin safiyar yau ya hada da motoci biyu, wata farar motar Toyota Hiace mai lamba FKJ 095 XE da kuma Honda Accord. Motar Saloon, wacce ba za a iya tantance lambar rajista ba.

“Mutane tara ne suka kone kurmus a wani mummunan hatsarin da ya afku a hanyar Ore-Lagos da sanyin safiyar yau. Hatsarin ya faru ne sakamakon fashewar taya, wanda ya yi sanadiyar yin karo da juna, wanda daga baya ya yi sanadin tashin gobara, wadda ta kone dukkan mutanen da ke cikin motocin da ba a iya gane su ba.” Inji shi.

Alonge ya ce an ajiye gawarwakin wadanda abin ya shafa a dakin ajiye gawa na babban asibitin Ore.

Ya shawarci masu ababen hawa da su rika kiyaye kayyakin gudu, su maida hankali, su yi hakuri, su kuma bi duk ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa yayin tuki domin ceton rayuka da dukiyoyi.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp