fidelitybank

Mutane 821 sun sayi fom din takarar majalisar wakilai ta sanata 241 a – APC

Date:

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ta tara biliyoyin Naira gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da wasu masu neman mukamai daban-daban a zaben 2023 suka fitar da miliyoyin Naira don siyan fam din takarar jam’iyyar, inji rahoton Naija News Hausa.

APC ta sanar a ranar Talata mai zuwa a matsayin wa’adin sayen fom yayin da ta ke shirin tunkarar zaben fidda gwani.

Dangane da haka, akalla ’yan takarar gwamna 95 ne suka biya tare da karbar fom din tsayawa takara kafin yammacin ranar Alhamis.

A baya dai APC ta karbi kudi kimanin Naira biliyan 1.630 daga hannun ‘yan takarar shugaban kasa 17, ciki har da mace daya mai neman shugabancin kasar, wadanda suka karbi fom dinsu.

Naija News Hausa ta fahimci cewa, yayin da mazaje masu neman tsayawa takarar su biya Naira miliyan 100 kowannensu, an kuma umurci mace da ta biya Naira miliyan 30 kacal.

Domin kara wadatar da kudin jam’iyyar, jam’iyyar ta karbi kudi daga mutane 241 masu neman kujerun Sanata.

Haka kuma, kawo yanzu mutane 821 ne suka sayi fom din takarar majalisar wakilai.

Idan dai za a iya tunawa a ranar Alhamis din nan, jimillar ‘yan takara 1,505 da ke neman tikitin jam’iyyar a Majalisar Dokokin Jihohi 36 su ma sun biya tare da karbar fom dinsu.

Sakataren kungiyar APC na kasa, Sulaiman Arugugu ne ya bayyana hakan ga manema labarai a wata sanarwa da ya fitar jiya.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp