fidelitybank

Mutane 821 sun sayi fom din takarar majalisar wakilai ta sanata 241 a – APC

Date:

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ta tara biliyoyin Naira gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da wasu masu neman mukamai daban-daban a zaben 2023 suka fitar da miliyoyin Naira don siyan fam din takarar jam’iyyar, inji rahoton Naija News Hausa.

APC ta sanar a ranar Talata mai zuwa a matsayin wa’adin sayen fom yayin da ta ke shirin tunkarar zaben fidda gwani.

Dangane da haka, akalla ’yan takarar gwamna 95 ne suka biya tare da karbar fom din tsayawa takara kafin yammacin ranar Alhamis.

A baya dai APC ta karbi kudi kimanin Naira biliyan 1.630 daga hannun ‘yan takarar shugaban kasa 17, ciki har da mace daya mai neman shugabancin kasar, wadanda suka karbi fom dinsu.

Naija News Hausa ta fahimci cewa, yayin da mazaje masu neman tsayawa takarar su biya Naira miliyan 100 kowannensu, an kuma umurci mace da ta biya Naira miliyan 30 kacal.

Domin kara wadatar da kudin jam’iyyar, jam’iyyar ta karbi kudi daga mutane 241 masu neman kujerun Sanata.

Haka kuma, kawo yanzu mutane 821 ne suka sayi fom din takarar majalisar wakilai.

Idan dai za a iya tunawa a ranar Alhamis din nan, jimillar ‘yan takara 1,505 da ke neman tikitin jam’iyyar a Majalisar Dokokin Jihohi 36 su ma sun biya tare da karbar fom dinsu.

Sakataren kungiyar APC na kasa, Sulaiman Arugugu ne ya bayyana hakan ga manema labarai a wata sanarwa da ya fitar jiya.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp