fidelitybank

Mutane 81 ne suka mutu wanda aka jefawa bam a Kaduna – Sojoji

Date:

Hedikwatar tsaro ta Najeriya ta ba da tabbacin mutuwar mutum 81 sakamakon harin kuskure da wani jirgin sojin Najeriya ya kai kan farar hula a Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna a arewacin Najeriya.

Manjo Janar Edward Buba, Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron ne ya bayyana haka inda ya ce mutum 70 ne suka jikkata sakamakon harin.

A baya dai, hukumar ba da agajin gaggawa ta ba da rahoton cewa sama da mutum 85 ne suka mutu sakamakon harin da aka kai, yayin da wasu ƙungiyoyi ke cewa adadin mutanen da suka mutu ya zarce haka.

Hedikwatar tsaron ta kuma ce daga yanzu, za ta tabbatar da inda za ta kai hari ɗari-ɗari kafin jefa bom.

“Za mu ci gaba da aiwatar da ayyukanmu bisa ƙa’idojin aiki wanda hakan muke yi,”

“Game da abin da ya faru a Kaduna, sojoji sun ɗauki darasi kuma za su ci gaba da aiki da shi. Za mu tabbatar ba a sake ganin irin haka ba a gaba.”

Janar Buba ya kuma mayar da martani game da zarge-zargen da wata ƙungiyar arewa ta yi cewa an kai harin ne domin rage yawan al’ummar arewa inda ya ce “rundunar sojin Najeriya ta ƙunshi ma’aikata daga kowace ƙabila a Najeriya. Ko ma me ƙungiyar ta ce, harin ya faru ne a kan kuskure.”

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp