fidelitybank

Mutane 80,000 ne za su zana jarabawa a ranar 6 ga wata – JAMB

Date:

Kusan mutum 80,000 ne za su rubuta jarrabawar JAMB da aka sake tsara rubutawa ranar 6 ga watan Mayu.

A cikin wata sanarwa da shugaban sashen hulɗa da jama’a na hukumar Fabian Benjamin ya fitar, ya ce an samu jinkirin ne sakamakon aikin tantance sakamakon jarrabawar da aka rubuta.

Sanarwar ta ce ɗaliban da aka tantance a cibiyoyin rubuta jarrabawar, amma ba su rubuta jarrabawar ba, da waɗanda ba a tantance bayanansu ba, da waɗanda aka samu saɓanin bayanansa za su samu saƙonnin rubuta jarrabawar.

Sanarwar ta ce “Waɗanda suka samu matsaloli a lokacin rubuta jarrabawarsu, ba za su ga sakamakonsu ba, a maimakon haka za su samu saƙon sake rubuta jarrabawar.

Hukumar ta ce sakamakon zaman gaggawa da ta yi ranar 30 ga watan Afrilu, ta saka ranar 6 ga watan Mayu a matsayin ranar da za a sake rubuta jarrabawar ga waɗanda ba su rubuta jarrabarwa ba.

Sanarwar ta kuma yi kira ga ɗaliban da abin ya shafa su fitar da takardun bayanansu na jarrabawar tsakanin 4 zuwa 5 ga watan Mayu, domin sanin lokaci da kuma wurin da za su rubuta jarrabawar.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp