Akalla mutane ashirin da takwas ne rahotanni suka ce sun mutu a wani hatsarin jirgin ruwa da ya afku a jihar Sokoto.
Rahotanni sun bayyana cewa, wadanda abin ya rutsa da su na tafiya ne zuwa yankunan da ke makwabtaka da su domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum, yayin da kwale-kwalen da ke dauke da fasinjoji kusan 34 ya kife.
Naija News ta rawaito cewa, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Laraba a kauyen Magana da ke karamar hukumar Shagari.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, hakimin kauyen Gidan-Magana, Mohammed Auwalu, ya ce, tuni aka binne gawarwakin wadanda suka mutu kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Da yake mayar da martani kan hadarin, sakataren karamar hukumar Shagari, Mas’oud Shagari, ya ce sama da gawarwaki 26 ne aka zakulo daga kogin yayin da ake ci gaba da neman wadanda suka tsira da ransu.