fidelitybank

Mutane 8 sun ƙone ƙurmus sakamakon fashewar tamkar mai a Ondo

Date:

Kimanin mutum takwas ne aka tabbatar sun mutu, sakamakon fashewar wata tankar dakon mai a jihar Ondo.

Lamarin ya ƙazance ne yayin da wuta ta kama a daidai lokacin da mazauna garin ke diban mai daga tankar da ta yi hatsarin a daren ranar Lahadi.

Rundunar ‘yan sandan jihar Ondo ta ce motar dakon man ta faɗi ne a kan titi, inda kusan dukkanin abubuwan da ke cikinta ya malale. Bayan haka ne mazauna yankin suka mamaye wurin domin dibar man.

“Motar tankar ta fashe inda ta kashe mutum takwas, ta kuma raunata wasu da dama wadanda aka garzaya da su asibiti, kamar yadda kakakin ‘yan sandan ya shaida wa BBC.

Mazauna yankin da shaidun gani da ido sun ce tankar ta fashe ne a wata unguwa da ke kusa da gidan mai, da kuma wani ginin coci amma babu ko daya da gobarar ta shafa.

Najeriya dai na fuskantar karin kusan kashi 400 na farashin man fetur tun watan Yuni bayan cire tallafin man da shugaba Bola Tinubu ya yi, matakin da ya ƙara iza wutar tsadar rayuwa da tsadar kayan masarufi.

Ƙasar wadda ta fi kowacce ƙarfin tattalin arziƙi a Afirka tana shigo da sama da kashi 90 cikin 100 na man da take bukata saboda gaza tace danyen mai a cikin gida saboda lalacewar matatun mai mallakin gwamnati

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp