fidelitybank

Mutane 6 sun mutu bayan sun taka nakiyar Boko Haram a Borno

Date:

Akalla mutane shida ne suka mutu a Borno, lokacin da wata motar sufuri ta bi ta kan wata boyayyiyar nakiya da ‘yan ta’addar Boko Haram suka binne.

Lamarin ya faru ne a kan hanyar karkara da ke tsakanin Bama zuwa Kawuri a karamar hukumar Konduga, inda jama’a suka saba tafiya zuwa wasu sassan jihar.

Mota kirar Toyota starlet da ta dawo daga jihar Adamawa ta taka bam din, inda ta kashe fasinjoji biyar da ke cikin jirgin.

Direban da ya samu munanan raunuka, ya mutu bayan sa’a guda a wani asibiti a Maiduguri.

Hanyar da ke tsakanin garin Bama zuwa Konduga ta kasance cikin kwanciyar hankali da lumana domin ba a samu wani hari ba a cikin shekaru 6 da suka gabata sai da maharan suka yanke shawarar tayar da bama-bamai a kan titin.

Mazauna Maiduguri sun ce sun yi mamakin yadda al’amura ke faruwa a baya-bayan nan, ganin yadda ayyukan ta’addanci ke kara zama sabon salo duk da kiran da gwamnati ta yi na mika wuya.

Idan dai za a iya tunawa gwamnati ta ce sama da ‘yan ta’adda dubu dari tare da iyalansu ne suka mika wuya duk da haka adadin hare-haren na baya-bayan nan na nuni da cewa akwai bukatar a yi da gaske dangane da ayyukan ta’addanci musamman a jihar Borno.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp