Hukumar kare haƙƙin ɗan’adam a Najeriya ta ce, adadin mutum ɗari biyar da saba’in (570) aka kashe a watan Afrilun bana, a cewar wani sabon rahoto da ta fitar.
Hukumar ta kuma ce mutum ɗari biyu da saba’in da takwas (278) aka yi garkuwa da su daga alƙaluman da ta tattara.
A shafinta na intanet, hukumar ta ce ta tattara alƙaluman ne daga koken da ta samu na keta haƙƙin ɗan adam daga ofisoshinta da ke sassan Najeriya.
Rahoton dai ya yi nazari ne tun daga watan Janairun 2025, zuwa watan Afrilun shekarar.