fidelitybank

Mutane 52 ne suka mutu a harin Filato

Date:

Waɗanda suka rasu a harin da wasu mahara suka kai a ƙaramar hukumar Bokkos na jihar Filato da ke Najeriya sun ƙaru zuwa 52, kamar yadda ƙungiyar ci gaban al’adun Bokkos ta bayyana.

Shugaban ƙungiyar, Farmasum Fuddang ne ya bayyana wa tashar Channels haka, inda ya ce an binne mutum 31 a rami ɗaya a ranar Alhamis, sannan akwai wasu guda biyar da suka ƙone a ƙauyen Hurti, sai kuma wasu guda 11 a ƙauyen Ruwi, da wasu guda huɗu a ƙauyen Manguna, da kuma wani mutum a ƙauyen Daffo.

A nata ɓangaren, gwamnatin jihar Filato ta yi kira ga ƴan jihar su kwantar da hankalinsu a daidai lokacin da ake cigaba da neman waɗanda ba a gani ba.

Kwamishinar watsa labarai ta jihar, Joyce Remnap ta ce an tura jami’an tsaro yankunan domin tabbatar da zaman lafiya ya wanzu.

“Sannan an kama wasu waɗanda ake zargi suna da hannu a kashe-kashen,” in ji ta, sannan ta ƙara da cewa, “muna kira da a guji ɗaukar doka a hannu.”

Tun a farkon harin ne dai ƙungiyar makiyaya ta Gan Allah ta fito ta ce maharan ba fulani ba ne, kuma ba su da wata alaƙa da su.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp