Waɗanda suka rasu a harin da wasu mahara suka kai a ƙaramar hukumar Bokkos na jihar Filato da ke Najeriya sun ƙaru zuwa 52, kamar yadda ƙungiyar ci gaban al’adun Bokkos ta bayyana.
Shugaban ƙungiyar, Farmasum Fuddang ne ya bayyana wa tashar Channels haka, inda ya ce an binne mutum 31 a rami ɗaya a ranar Alhamis, sannan akwai wasu guda biyar da suka ƙone a ƙauyen Hurti, sai kuma wasu guda 11 a ƙauyen Ruwi, da wasu guda huɗu a ƙauyen Manguna, da kuma wani mutum a ƙauyen Daffo.
A nata ɓangaren, gwamnatin jihar Filato ta yi kira ga ƴan jihar su kwantar da hankalinsu a daidai lokacin da ake cigaba da neman waɗanda ba a gani ba.
Kwamishinar watsa labarai ta jihar, Joyce Remnap ta ce an tura jami’an tsaro yankunan domin tabbatar da zaman lafiya ya wanzu.
“Sannan an kama wasu waɗanda ake zargi suna da hannu a kashe-kashen,” in ji ta, sannan ta ƙara da cewa, “muna kira da a guji ɗaukar doka a hannu.”
Tun a farkon harin ne dai ƙungiyar makiyaya ta Gan Allah ta fito ta ce maharan ba fulani ba ne, kuma ba su da wata alaƙa da su.