Fashewar tukunyar iskar gas a wurin haƙar ma’adinai a gabashin Iran ta kashe mutane aƙalla 51, kamar yadda kafar yaɗa labaran ƙasar ta bayyana a ranar Lahadi.
Fiye da wasu 20 ne kuma suka jikkata bayan fashewar a lardin Khorasan ta Kudu.
An ruwaito cewa fashewar ta sinadarin methane ta afku a wasu sassa biyu na wurin haƙar ma’adinan a garin Tabas mai tazarar kilomita 540 a kudu maso gabashin Tehran, babban birnin ƙasar.
Fashewar ta afku ne da misalin karfe 9:00 agogon ƙasar a ranar Asabar, kamar yadda kafofin yaɗa labaran ƙasar suka bayyana.
Gwamnan Kudancin Khorasan, Javad Ghenaatzadeh ya ce akwai ma’aikata 69 a wurin lokacin da aka samu fashewar.
Kamfanin dillancin labarai na AP, ya ce: “An samu fashewar wani abu kuma abin takaici mutum 69 ne ke aiki a wurin haƙar ma’adinan a Madanjoo.
“Akwai mutane 22 a sashe na farko na wurin, sannan mutum 47 a ɗaya sassan.”
Har yanzu dai ba a san adadin mutanen da suka rage a raye ba da kuma waɗanda suka maƙale a wurin haƙar.