fidelitybank

Mutane 51 sun mutu a wata fashewa a wurin haƙar ma’adinai a Iran

Date:

Fashewar tukunyar iskar gas a wurin haƙar ma’adinai a gabashin Iran ta kashe mutane aƙalla 51, kamar yadda kafar yaɗa labaran ƙasar ta bayyana a ranar Lahadi.

Fiye da wasu 20 ne kuma suka jikkata bayan fashewar a lardin Khorasan ta Kudu.

An ruwaito cewa fashewar ta sinadarin methane ta afku a wasu sassa biyu na wurin haƙar ma’adinan a garin Tabas mai tazarar kilomita 540 a kudu maso gabashin Tehran, babban birnin ƙasar.

Fashewar ta afku ne da misalin karfe 9:00 agogon ƙasar a ranar Asabar, kamar yadda kafofin yaɗa labaran ƙasar suka bayyana.

Gwamnan Kudancin Khorasan, Javad Ghenaatzadeh ya ce akwai ma’aikata 69 a wurin lokacin da aka samu fashewar.

Kamfanin dillancin labarai na AP, ya ce: “An samu fashewar wani abu kuma abin takaici mutum 69 ne ke aiki a wurin haƙar ma’adinan a Madanjoo.

“Akwai mutane 22 a sashe na farko na wurin, sannan mutum 47 a ɗaya sassan.”

Har yanzu dai ba a san adadin mutanen da suka rage a raye ba da kuma waɗanda suka maƙale a wurin haƙar.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp