fidelitybank

Mutane 5 sun mutu 60 na kwance a jihar Legas sakamakon cutar Kwalara

Date:

Akalla mutane biyar ne suka mutu sannan wasu 60 kuma suna kwanta a asibiti, sakamakon barkewar cutar kwalara a kewayen yankin Eti Osa da Island da Ikorodu da Kosofe na jihar Legas.

Kwamishinan lafiya na jihar Legas, Akin Abayomi, ne ya bayyana hakan yayin da yake mayar da martani game da barkewar cutar.

Abayomi ya ce gwamnatin jihar ta fitar da wani kira na a kara sanya ido tare da daukar matakan kariya, domin dakile bazuwar cutar kwalara a jihar.

Ya kara da cewa, abin bakin ciki, an samu rahoton mutuwar mutane biyar musamman daga majinyatan da suka makara tare da matsanancin rashin ruwa a jikin su.

Kwamishinan ya kara da cewa, biyo bayan ruwan sama da aka yi a baya-bayan nan, jihar Legas ta samu karuwar masu fama da matsananciyar amai da gudawa, inda y ace, matsugunan birane da cunkoson jama’a da rashin tsaftar muhalli na cikin hadari.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp