fidelitybank

Mutane 39 sun kamu da cutar kyandar Biri a Najeriya – Ministan Lafiya

Date:

Gwamnatin tarayya, ta ce, ta tsaurara matakan bincike a dukkan hanyoyin shigarta domin daƙile yiwuwar shiga da cutar ƙyandar Biri cikin ƙasar nan.

Wannan na zuwa ne bayan hukumar hana yaɗuwar cutuka ta Afirka, da ma Majalisar Dinkin Duniya sun ƙaddamar da dokar ta ɓaci a kan yaƙi da cutar ta ƙyandar Biri da ake kira da Mnkey pox.

Da yake sanar da matakan da hukumomi a a kasar nan ke ɗauka domin kare jama’a daga wannan cuta, ministan lafiya Farfesa Muhammad Pate, ya ce, za a tsaurara bincike a kan masu shiga Najeriya daga kowanne ɓangare, domin tabbatar da ganin wani daga waje bai shigar da ƙwayar cutar cikin ƙasar ba.

Sanarwar da Ministan ya fitar ta ce cibiyar daƙile yaɗuwar cutuka ta ƙasar ta sanar da gwamnati da cewa an samu mutum 39 da suka kamu da cutar ƙyandar Biri a Najeriya.

Ministan ya ce daga alƙalumman da hukumomi suka tattara daga farkon wannan shekarar, an samu masu cutar ne a jihohi 33 da birnin tarayya Abuja, kuma kawo yanzu babu wanda ya mutu sanadiyyar cutar.

Saboda haka ne ministan ya ce gwamnati ta yi saurin samar da tsarin yin gwaji ga duk wanda zai shiga Najeriya, domin gano cutar tun kafin a shigar masu da annoba.

Itama hukumar hana yaduwar cutuka ta Najeriyar ta jaddada wannan matakin da gwamnatin tarayyar ta sanar, kuma shugaban ta Dr Jide Idris, ya yi bayanin cewa sun ƙara matakan yin gwaji a filayen jiragen saman ƙasa da ƙasa guda 5 da ake da su a ƙasar, da tashoshin ruwa 10 da kuma iyakokin kan ƙasa guda 51, duk dai a ƙoƙarin hana shiga da cutar.

Hukumomi a Najeriyar dai sun kuma sanar da tsaurara matakan tantance masu ɗauke da cutar a jihohin Legas da Enugu da Rivers da Cross Rver da Akwa Ibom da kuma Adamawa.

Sauran jihohin sun haɗa da Taraba da Kano da kuma birnin tarayya Abuja.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...
X whatsapp