Hukumar kiyaye aukuwar haɗura ta kasa, ta tabbatar da mutuwar mutum 37 a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babbar hanyar Damaturu zuwa maiduguri a yankin arewa maso gabashin ƙasar.
Babban jami’in hukumar mai lura da shiyya ta 12 ,wadda ta ƙunshi jihohin Bauchi, da Borno da Yobe ACM Rotimi Adeleye ya tabbatar wa da BBC faruwar lamarin.
Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne da safiyar ranar Talata.
Ya ce motoci biyu ne ƙirar ‘Hummer’ suka yi taho-mu-gama da juna, nan take kuma suka kama da wuta inda mutum 37 da ke cikin motocin suka mutu sakamkon ƙonewa da suka yi.
Jami’in ya ƙara da cewa gudun wuce-kima ne ya haddasa aukuwar hatsarin, inda ya yi kira ga direbobin ƙasar da su ƙaurace wa ɗabi’ar gudun wuce-sa’a yayin tuki.