Rundunar ƴansanda a jihar Kano, ta ce ta kama mutum 326 bisa zargin su da hannu a yamutsin da aka samu lokacin zanga-zangar matsin rayuwa a ranar Alhamis.
Rundunar ta ce cikin mutanen da ta kama akwai mata, da maza da kuma ƙananan yara.
Haka nan sun bayyana cewa an ƙwace bindiga ƙirara AK47.
Zanga-zangar lumanan da matasa suka shirya a faɗin ƙasar ta rikiɗe zuwa rikici a wasu jihohi, lamarin da ya kai ga sanya dokar ta ɓaci a jihohi biyar.
A Kano masu zanga-zanga sun ɓalle shaguna da ɓarnata kayan gwamnati a lokacin da lamarin ya yamutse.
Ƴansanda sun mayar da martani ta hanyar jefa wa masu zanga-zangar hayaƙi mai sa hawaye.
Haka nan an zargi jami’an tsaron da yin harbi da bindiga a cikin masu zanga-zanga, lamarin da ya yi sanadiyyar asarar rayuka.
Wani likta ya tabbatar wa BBC mutuwar mutum uku a jihar ta Kano