Majalisar tattalin arzikin ƙasa NEC, ta ce ambaliyar da ta auku a Najeriya a bana ta shafi ƙananan hukumomi 217 na jihohin Najeriya 34, inda aƙalla mutum 321 suka rasu.
NEC ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis, inda ta ƙara da cewa ambaliyar ta shafi aƙalla mutum 1,372,557, sannan ta raba aƙalla mutum 740,743 da muhallansu.
Gwamnan jihar Anambra, farfesa Chukwuma Soludo ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban ƙasa bayan taron na NEC, wana mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya jagoranta, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Ya ce ambaliyar ta jikkata mutum 2,854, ta ɓarnata gidaje 281,000, da kadada 258,000 na gonaki.