fidelitybank

Mutane 32 ne kawo yanzu suka mutu a harin Gwoza

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Kassim Shettima, ya ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren ƙunar baƙin wake da aka kai garin Gwoza a jihar Borno ya ƙaru zuwa 32.

Shekttima ya sanar da haka ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya zuwa jihar ta Borno game da ibtila’in da ya faru. Ya ƙara da cewa cikin mutum 42 da aka kai asibiti bayan harin, an sallami mutum 14.

A cewarsa, har yanzu mutum 26 na samun kulawar likitoci.

Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma bai wa dukkanin mutanen da ibtila’in ya rutsa da su tallafin kuɗi tare da yi wa iyalan waɗanda suka mutu jaje.

“Zuwa yanzu an samu mutum 32 da suka mutu, an kawo mutum 42 daga Gwoza kuma an sallami kimanin mutum 14 amma mutum 26 har yanzu suna jinya a asibiti.

“Ina amfani da wannan dama na miƙa godiya ga gwamnatin jihar Borno da hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa da ta jiha da kuma ƙungiyar ICRC saboda gudummawar da suka bayar,” in ji shi.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp