fidelitybank

Mutane 30 sun mutu an kwantar da dama a asibiti bayan sun sha giya a India

Date:

Aƙalla mutum talatin ne suka mutu aka kuma kwantar da gommai a asibiti bayan da suka sha wata giya haɗin gida a gundumar Kallakuruchi da ke jihar Tamil Nadu da ke kudancin Indiya.

Hukumomi sun ce yawancin waɗanda aka kwantar a asibitin sama da 80 suna fama ne da amai da gudawa da kuma ciwon ciki bayan sun sha giyar ta burkutu a ranar Talata da daddare.

An kama jami’ai goma da suka haɗa da wani babban jami’in haraji da Baturen ƴansanda a kan lamarin.

Babban minista na jihar ta Tamil Nadu, MK Stalin ya rubuta a shafinsa na sada zumunta da muhawara cewa lamarin ya girgiza shi.

Ministan ya kuma sanar da diyyar dala dubu 12 ga iyalan waɗanda suka mutu, su kuwa waɗanda aka kwantar a asibiti za a ba kowane mutum ɗaya dala 600.

KOwace shekara gomman mutane suna mutuwa a Indiya sakamakon shan giyar da ake yi ta gargajiya, inda yawanci ake sanya mata sinadarai da suka wuce kima.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp